Home

Music

Video

Kannywood
Tags:

DINO MALAYE YA MIQA KANSA GA YAN SANDA


Subscribe Our Channel

Rundunar 'yan sandan Najeriya ta tabbatar da cewa dan majalisar dattijan kasar mai wakiltar jihar Kogi ta Arewa, Dino Melaye yana hannunta.
Jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan Najeriya, Aremu Adeniran ya tabbatar
 cewa Sanata Melaye yana hannunsu.
Ya kuma ce shi ne ya mika kansa a safiyar Talata, kamar yadda ya bayyana a shafinsa na Twitter gabanin yin hakan.
Aremu Adeniran ya ce za su ci gaba da tsare Sanata Melaye har sai bayan sun kammala binciken da suke yi a kan zargin da ake yi masa.
A ranar Litinin ne dai 'yan sanda suka yi dirar mikiya a gidan dan majalisar a unguwar Maitama da ke Abuja bayan da jam'ian hukumar shige da fice suka kama shi yayin da yke shirin fita daga Najeriya.
Amma daga bisani an sako shi.
A kwanakin bayan ne rundunar 'yan sandan kasar ta bayyana dan majalisar dattawan a matsayin wanda suke nema ruwa-a-jallo.
'Yan sandan na zarginsa da kin bayyana a gaban kotu domin fuskantar shari'a kan zargin daukar nauyin wasu mutane su tayar da hankali da aikata miyagun laifuka.
Sai dai sanatan ya yi watsi da dukkan zarge-zargen yana mai cewa siyasa ce kawai.

Share this


0 comments:

Post a Comment

FG HAUSA | All Rights Are Reserved
Fb tt wp ig g+
Owned And Designed By ASSALAPHY